Hausa
Surah Al-'alaq ( The Clot ) - Aya count 19
اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَ 
( 1 ) 
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍ 
( 2 ) 
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
اقْرَأْ وَرَبُّكَ الْأَكْرَمُ 
( 3 ) 
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِ 
( 4 ) 
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
عَلَّمَ الْإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْ 
( 5 ) 
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
كَلَّا إِنَّ الْإِنسَانَ لَيَطْغَىٰ 
( 6 ) 
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
أَن رَّآهُ اسْتَغْنَىٰ 
( 7 ) 
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الرُّجْعَىٰ 
( 8 ) 
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَىٰ 
( 9 ) 
Shin, kã ga wanda ke hana.
عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰ 
( 10 ) 
Bãwã idan yã yi salla?
أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَىٰ 
( 11 ) 
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَىٰ 
( 12 ) 
Ko ya yi umurni da taƙawa?
أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ 
( 13 ) 
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ اللَّهَ يَرَىٰ 
( 14 ) 
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِ 
( 15 ) 
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍ 
( 16 ) 
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
فَلْيَدْعُ نَادِيَهُ 
( 17 ) 
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَ 
( 18 ) 
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِب ۩ 
( 19 ) 
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).