Hausa
Surah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) - Aya count 182
وَالصَّافَّاتِ صَفًّا 
( 1 ) 
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا 
( 2 ) 
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا 
( 3 ) 
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ 
( 4 ) 
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ 
( 5 ) 
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ 
( 6 ) 
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ 
( 7 ) 
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ 
( 8 ) 
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ 
( 9 ) 
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ 
( 10 ) 
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍ 
( 11 ) 
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ 
( 12 ) 
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ 
( 13 ) 
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ 
( 14 ) 
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ 
( 15 ) 
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ 
( 16 ) 
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ 
( 17 ) 
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ 
( 18 ) 
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ 
( 19 ) 
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ 
( 20 ) 
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ 
( 21 ) 
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ 
( 22 ) 
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ 
( 23 ) 
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ 
( 24 ) 
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ 
( 25 ) 
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ 
( 26 ) 
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ 
( 27 ) 
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ 
( 28 ) 
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ 
( 29 ) 
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ 
( 30 ) 
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ 
( 31 ) 
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ 
( 32 ) 
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ 
( 33 ) 
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ 
( 34 ) 
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ 
( 35 ) 
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ 
( 36 ) 
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ 
( 37 ) 
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ 
( 38 ) 
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ 
( 39 ) 
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ 
( 40 ) 
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ 
( 41 ) 
Waɗannan sunã da abinci sananne.
فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ 
( 42 ) 
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ 
( 43 ) 
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ 
( 44 ) 
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ 
( 45 ) 
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ 
( 46 ) 
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ 
( 47 ) 
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ 
( 48 ) 
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ 
( 49 ) 
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ 
( 50 ) 
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ 
( 51 ) 
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ 
( 52 ) 
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ 
( 53 ) 
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ 
( 54 ) 
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ 
( 55 ) 
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ 
( 56 ) 
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ 
( 57 ) 
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ 
( 58 ) 
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ 
( 59 ) 
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ 
( 60 ) 
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ 
( 61 ) 
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ 
( 62 ) 
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ 
( 63 ) 
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ 
( 64 ) 
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ 
( 65 ) 
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ 
( 66 ) 
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ 
( 67 ) 
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ 
( 68 ) 
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ 
( 69 ) 
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ 
( 70 ) 
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ 
( 71 ) 
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ 
( 72 ) 
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ 
( 73 ) 
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ 
( 74 ) 
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ 
( 75 ) 
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ 
( 76 ) 
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ 
( 77 ) 
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ 
( 78 ) 
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ 
( 79 ) 
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ 
( 80 ) 
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ 
( 81 ) 
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ 
( 82 ) 
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ 
( 83 ) 
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ 
( 84 ) 
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ 
( 85 ) 
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ 
( 86 ) 
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ 
( 87 ) 
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ 
( 88 ) 
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ 
( 89 ) 
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ 
( 90 ) 
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ 
( 91 ) 
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ 
( 92 ) 
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ 
( 93 ) 
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ 
( 94 ) 
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ 
( 95 ) 
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ 
( 96 ) 
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ 
( 97 ) 
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ 
( 98 ) 
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ 
( 99 ) 
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ 
( 100 ) 
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ 
( 101 ) 
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ 
( 102 ) 
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ 
( 103 ) 
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ 
( 104 ) 
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ 
( 105 ) 
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ 
( 106 ) 
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ 
( 107 ) 
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ 
( 108 ) 
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ 
( 109 ) 
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ 
( 110 ) 
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ 
( 111 ) 
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ 
( 112 ) 
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ 
( 113 ) 
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ 
( 114 ) 
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ 
( 115 ) 
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ 
( 116 ) 
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ 
( 117 ) 
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ 
( 118 ) 
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الْآخِرِينَ 
( 119 ) 
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
سَلَامٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ 
( 120 ) 
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ 
( 121 ) 
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ 
( 122 ) 
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ 
( 123 ) 
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلَا تَتَّقُونَ 
( 124 ) 
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ 
( 125 ) 
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ 
( 126 ) 
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ 
( 127 ) 
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ 
( 128 ) 
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ 
( 129 ) 
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
سَلَامٌ عَلَىٰ إِلْ يَاسِينَ 
( 130 ) 
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ 
( 131 ) 
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ 
( 132 ) 
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَ 
( 133 ) 
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ 
( 134 ) 
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ 
( 135 ) 
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ 
( 136 ) 
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ 
( 137 ) 
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
وَبِاللَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ 
( 138 ) 
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ 
( 139 ) 
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ 
( 140 ) 
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ الْمُدْحَضِينَ 
( 141 ) 
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ 
( 142 ) 
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ 
( 143 ) 
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ 
( 144 ) 
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌ 
( 145 ) 
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ 
( 146 ) 
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ 
( 147 ) 
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ 
( 148 ) 
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ 
( 149 ) 
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ 
( 150 ) 
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
أَلَا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ 
( 151 ) 
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ 
( 152 ) 
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَ 
( 153 ) 
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ 
( 154 ) 
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
أَفَلَا تَذَكَّرُونَ 
( 155 ) 
Shin, bã ku tunãni?
أَمْ لَكُمْ سُلْطَانٌ مُّبِينٌ 
( 156 ) 
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ 
( 157 ) 
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ 
( 158 ) 
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ 
( 159 ) 
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ 
( 160 ) 
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ 
( 161 ) 
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
مَا أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَاتِنِينَ 
( 162 ) 
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِ 
( 163 ) 
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
وَمَا مِنَّا إِلَّا لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ 
( 164 ) 
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَ 
( 165 ) 
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَ 
( 166 ) 
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
وَإِن كَانُوا لَيَقُولُونَ 
( 167 ) 
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ الْأَوَّلِينَ 
( 168 ) 
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ 
( 169 ) 
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
فَكَفَرُوا بِهِ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ 
( 170 ) 
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَ 
( 171 ) 
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
إِنَّهُمْ لَهُمُ الْمَنصُورُونَ 
( 172 ) 
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَ 
( 173 ) 
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ 
( 174 ) 
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ 
( 175 ) 
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ 
( 176 ) 
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَ 
( 177 ) 
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ 
( 178 ) 
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ 
( 179 ) 
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ 
( 180 ) 
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
وَسَلَامٌ عَلَى الْمُرْسَلِينَ 
( 181 ) 
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ 
( 182 ) 
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.