Hausa
Surah At-Takwir ( The Overthrowing ) - Aya count 29
إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ 
( 1 ) 
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ 
( 2 ) 
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ 
( 3 ) 
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ 
( 4 ) 
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ 
( 5 ) 
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ 
( 6 ) 
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ 
( 7 ) 
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْ 
( 8 ) 
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ 
( 9 ) 
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ 
( 10 ) 
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ 
( 11 ) 
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ 
( 12 ) 
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ 
( 13 ) 
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ 
( 14 ) 
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ 
( 15 ) 
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
الْجَوَارِ الْكُنَّسِ 
( 16 ) 
Mãsu gudu suna ɓũya.
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ 
( 17 ) 
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ 
( 18 ) 
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ 
( 19 ) 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ 
( 20 ) 
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ 
( 21 ) 
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ 
( 22 ) 
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ 
( 23 ) 
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ 
( 24 ) 
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ 
( 25 ) 
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ 
( 26 ) 
Shin, a inã zã ku tafi?
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ 
( 27 ) 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ 
( 28 ) 
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
وَمَا تَشَاءُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ 
( 29 ) 
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.